Gwamnonin da aka zaÉ“a a Æ™arÆ™ashin jam’iyyar PDP sun bayyana cewa ba za su yi haÉ—aka ko kawance da wata jam’iyya ta daban ba gabanin zaÉ“en 2027.
Gwamnonin sun bayyana matsayinsu ne a cikin wata sanarwa da suka fitar a ranar Litinin bayan wata ganawa da suka gudanar a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.
Tattaunawa kan yiwuwar haÉ—a kai don kalubalantar jam’iyyar APC na Æ™ara É—aukar hankali yayin da zaÉ“en 2027 ke Æ™aratowa.
Haka kuma, ’yan adawa sun fara gudanar da wasu “taruka masu mahimmanci” a wannan fanni.
ÆŠaya daga cikin manyan masu goyon bayan haÉ—akar jam’iyyu shi ne Atiku Abubakar, É—an takarar shugaban Æ™asa na PDP a zaÉ“en 2023.
Atiku Abubakar yana ci gaba da kira ga jam’iyyun adawa su haÉ—u kafin zaÉ“en 2027 domin su kwace mulki daga hannun gwamnatin APC Æ™arÆ™ashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu.
“Domin la’akari da jita-jita da ke yawo a faÉ—in Æ™asa game da yiwuwar haÉ—akar jam’iyyu, Æ™ungiyoyi da sauransu, taron ya yanke shawarar cewa PDP ba za ta shiga kowace irin haÉ—aka ko kawance ba,” in ji sanarwar.
Sai dai gwamnonin sun ce PDP na maraba da kowace jam’iyya, mutum ko Æ™ungiya da ke da niyyar shiga jam’iyyar domin kwace mulki daga APC a 2027.